✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sudais ya bai wa Mahir hutun limanci a Masallacin Harami

A jiya Juma'a ne dai Seikh Maher ya fadi lokacin da yake tsaka da karanta Suratul Fatiha.

Babban Limamin Masallatan Harami, Sheikh Abdurrahman al Sudais, ya bai wa Sheikh Maher Almu’aikali hutun limancin Sallar Asuba da Azahar a ranar Asabar sakamakon suma da ya yi a jiya Juma’a yana tsaka da jan Sallar Juma’a.

Sudais ya kuma bai wa Maher din umarnin hutawa a gida, har zuwa lokacin da zai warke daga rashin lafiyar da ke damunsa.

A jiya Juma’a ne dai Seikh Maher ya fadi lokacin da yake tsaka da karanta Suratul Fatiha yayin Sallar Juma’a, inda sheikh Sudais ya yi wuf ya karbi jagorancin sallar.

Daga baya dai shafin Haramain Sharifain ya rawaito cewa Mahir ya samu sauki, amma ba zai iya karasa Sallar Juma’ar ba.