✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Wata hajiyar Najeriya daga Filato ta rasu a Makkah

Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a sakamakon cutar suga a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya

Wata hajiyar Najeriya daga Jihar Filato ta rasu a birnin Makkah na ƙasar Saudiyya.

Hajiya Jamila Muhammad ta rasu ne a yayin da alhazai ke shirin fara gudanar da aikin Hajji gadan-gadan.

Sakataren Hukumar Kin Dadin Alhazai ta Jirage Filato, Daiyabu Dauda, ya sanar a ranar Litinin cewa Hajiya Jamila ta rasu ne a asibitin Sarki Abdulaziz da ke Makkah, sakamakon tashin cutar suga.

Ya ce Amirul Hajj na jihar da wasu manyan jami’ai sun halarci jana’izar marigayiyar, kamar yadda Musulunci ta tanada.

Da rayuwarta, yawan alhazan Najeriya da suka rasu a aikin Hajjin bana ya ƙaru zuwa mutum uku.

Kafin ita, Najeriya ta rsa alhazai biyu da suka hada da Hajiya Adizatu Dazumi daga Jihar Edo da kuma  Alhaji Saleh Saleh daga Jihar Abiya.