✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ranar Talata Tinubu zai yi wa Majalisar Dinkin Duniya jawabi

Wannan ne karon farko da shugaban zai yi jawabi ga babban zauren

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gabatar da jawabinsa a ranar Talata ga taron Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya karo na 78 a birnin New York na Amurka.

Ranar dai ita ce za ta zama ya farko a taron na bana, kuma wannan shi ne karo na farko da zai halarci taron a matsayin Shugaban Najeriya.

Kakakin shugaban, Ajuri Ngelale ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Asabar.

Ya ce ana sa ran shugaban zai bar Abuja zuwa birnin na New York ranar Lahadi, kwana daya bayan dawowarsa daga taron G-20 a kasar Indiya.

Yayin tafiyar dai, Tinubu zai samu rakiyar Gwamnoni Umo Eno (Akwa Ibom); Mohammed Inuwa Yahaya (Gombe State); Hope Uzodinma (Imo); Uba Sani (Kaduna); AbdulRahman AbdulRazak (Kwara) da kuma Seyi Makinde (Oyo).

Kazalika, shugaban zai samu rakiyar Shugaban ma’aikatan fadarsa, Femi Gbajabiamila da ministocinsa, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar (Harkokin Waje); Wale Edun (Kudi da Tattalin Arziki); Dr Mohammed Pate (Lafiya); Abubakar Badaru (Tsaro); sai Dele Alake (Ma’adinai).

Kazalika, a cikin ’yan tawagar akwai Ministar Walwala da Yaki da Talauci, Dr Betta Edu da na Masana’antu da Kasuwanci da Zuba Jari, Dr Doris Uzoka-Anite.

Mai ba Shugaban Kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu da kuma Shugabar Hukumar da ke kula da ’yan Najeriyar da ke kasashen waje (NIDCOM) Abike Dabiri-Erewa da sauran kusoshin gwamnati za su kasance a cikin tawagar.