✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Nada mukamin Karamin Minista ya saba wa tsarin mulki — Keyamo

Karamin Minista ba shi da wani iko na a zo a gani.

Karamin Ministan Kwadago da Ayyuka mai barin-gado, Festus Keyamo (SAN), ya gaya wa Shugaba Muhammadu Buhari mai barin-gado cewa nada mukamin Karamin Ministan ya saba wa tsarin mulkin kasar.

Keyamo wanda babban lauya ne a Najeriya ya fadi hakan ne a jiya Laraba, lokacin da yake gabatar da jawabinsa a zaman majalisar zartarwa na ban-kwana domin kawo karshen majalisar, wanda Shugaba Buhari ya jagoranta a Abuja.

Karamin ministan ya nuna cewa wannan mukami da ake bai wa mutane yawanci da sunan gwamnatin hadin kan kasa kusan ba ya aiki a zahiri ga yawancin wadanda ake nadawa a matsayin.

Domin ba wani iko na a-zo-a-gani da suke da shi, lamarin da a wani lokacin ma yake hada su rigima da wanda yake matsayin ainihin matsayin ministan.

Ya ce yawancin wadanda gwamnatocin baya suke nadawa a wannan mukami sun ki fitowa su yi magana ne saboda kar a ga ba su gode wa shugabannin kasar da suka ba su mukamin ba.

Festus Keyamo shi ne kakakin rusasshen kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu da Shettima.