✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za mu gurfanar da masu yi wa zaman lafiya barazana a Kaduna- El-Rufai

Gwamnan jihar Kaduna Nasir Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa , gwamnati zata gurfanar da duk masu yi wa zaman lafiya barazana a jihar. Gwamnan ya…

Gwamnan jihar Kaduna Nasir Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa , gwamnati zata gurfanar da duk masu yi wa zaman lafiya barazana a jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wani taro da hukumar zaman lafiya ta jihar ta shirya akan hanyoyin gudanar zaben 2019 cikin lumana a jihar.

El-Rufai, ya ce, idan har hukumar zabe mai zaman kanta ta gudanar da sahihin zabe kamar na zaben Gwamnan  jihar Osun, za a samu zaman lafiya a Kaduna lokacin zaben 2019 da bayan zaben.