✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a tafka mamakon ruwan sama a Kano, Sakkwato da wasu Jihohi 20 – NiMet

Za a fara tafka ruwan ne daga ranar Juma’a mai zuwa

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi hasashen za a tafka mamakon ruwan sama a Kano da Sakkwato daga ranar Juma’a.

Hukumar ta kuma ce za a sha ruwan a karin Jihohi 20, kamar yadda ta fitar a wani rahoto da ta fitar ranar Alhamis.

NiMet ta ce a lokacin hasashen, za a tafka mamakon ruwan na tsawon awa 24, kuma za a iya samun tsawa da ’yar kwarya-kwaryar ambaliyar ruwa da iska da walkiya da kuma ambaliya.

A cewar hasashen, za a fuskanci ’yar karamar ambaliya ranar Asabar a Jihohin Ribas da Delta da Bayelsa da Akwa Ibom da Kuros Riba da Yobe da Binuwai da Jigawa da Kano da Katsina da Zamfara da kuma Sakkwato.

“A jihohin Borno da Bauchi da Kaduna da Neja kuwa, akwai barazanar samun ruwan sama kadan-kadan. Dukkan ragowar Jihohin kuma ko dai ba za a sami ruwan ba ko kuma kadan za a yi,” in ji sanarwar.

Ga cikakkun jihohin da za a samu ruwan saman:

Sakkwato

Zamfara

Katsina

Kano

Bauchi

Kaduna

Filato

Oyo

Kogi

Nasarawa

Binuwai

Adamawa

Taraba

Kuros Riba

Imo

Ondo

Edo

Delta

Bayelsa

Ribas