✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a iya buga wasu wasannin cin Kofin Duniya na 2022 a Kuwait – Infantino

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino ya ce akwai yiwuwar a buga wasu wasannin cin Kofin Duniya a kasar Kuwait a shekarar…

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino ya ce akwai yiwuwar a buga wasu wasannin cin Kofin Duniya a kasar Kuwait a shekarar 2022 da za a yi a kasar Katar.

Infantino ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci Kuwait don kallon wasan karshe na gasar Yariman Kuwait inda ya shaida wa manema labarai cewa, za a iya buga wasu wasannin gasar ta FIFA ta 2022 a Kuwait.

Infantino ya ce, ya yi wuri a kawo batun kara yawan kungiyoyi daga 36 zuwa 48 inda ya ce matukar hakan ta tabbata to za a samu karin mahalarta gasar daga Nahiyar Asiya.

Shugaban na FIFA ya ce ya ji dadi da samun kungiyar kwallon kafa ta mata ta farko a Kuwait kuma ya kamata dukan kasashen yankin su yi koyi da Katar.