✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan Najeriya na da isasshen abinci a rumbunansu —Minista

Ya ce sam babu wata barazanar yunwa a Najeriya a bana

Ministan Noma da Raya Karkara, Mohammed Mahmud Abubakar ya ce babu wata barazanar yunwa a Najeriya saboda mutane na da isasshen abinci a rumbunansu.

Ya ba da tabbacin ne a Abuja ranar Litinin, yayin jawabi kan nasarorin gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari karo na biyar.

Da yake amsa tambaya a kan hauhawar farashin kayayyaki, Ministan ya ce, “Hakika muna da wadataccen abinci a kasar nan. Babu barazanar yunwa. Na yarda farashinsu ya tashi, amma gwara tashin farashi da a ce babu ne gaba daya.

“Muna noma isasshiyar shinkafa, mu ne ma na daya a nahiyar Afirka wajen nomanta, haka ma abin yake a fannin rogo da doya.

“A bangaren noman dawa kuwa, mu ne na biyu a duniya bayan Amurka, kuma na uku a noman gero a duniya. Muna da isasshen abinci, kuma ba za mu fuskanci karancinsa ba.”

Sai dai Ministan ya alakanta tsadar takin zamanin da ake fama da ita a bana kan annobar COVID-19 da sauyin yanayi da kuma rikicin Rasha da Ukraine.

Mohammed ya kuma ce a ranar 12 ga watan Disamba mai zuwa Gwamnatin Tarayya za ta gudanar da wani taron shiyya-shiyya kan rikicin manoma da makiyaya.

Ya kuma ce Gwamnatin za ta ci gaba da aikin gina rugage da burtalolin kiwo na zamani ga makiyaya.

A cewarsa, tuni aka riga aka ware wurare 16 a jihohi takwas a matsayin cibiyoyin kiwon dabbobi na kasa, kamar yadda yake kunshe a Daftarin Kiwon Dabbobi na Kasar (NLTP).