✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun sace hakimi da manoma 2 a Kaduna

Rahotanni sun bayyana cewar an sace hakimin ne lokacin da yake dawowa daga gona.

’Yan Bindiga sun yi garkuwa da Hakimin Tunburku, Malam Ashiru Sherehu da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewar, maharan sun yi awon gaba da Sherehu a kan hanyarsa ta dawowa daga gona a ranar Asabar.

’Yan bindiga sun addabi yankin da ke gundumar Fatika a ‘yan kwanakin nan da hare-hare.

A cewar wani mazaunin yankin, Ahmadu, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu da ke da nisan kilomita kaɗan daga garin saboda tsoron kada a kashe su ko kuma a sace su.

Wani basaraken gargajiya a yankin kuma Sarkin Fadan Galadimawa, Husseini Umar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an yi garkuwa da hakimin ƙauyen da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Asabar.

“Yana dawowa daga gonarsa da ke Tunburku sai ‘yan bindigar suka tare shi suka tafi da shi. Har yanzu ba mu ji daga gare su ba; kuma ba su tuntuɓe mu ba,” in ji shi.

A cewar Hussaini, an kuma sace wasu manoma biyu a yankin Sabon Layi da ke gundumar Kidandan a lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar Lahadi da rana.

Ya bayyana cewar mutanen ƙauyen da lamarin ya faru a gabansu sun kasa yin komai saboda ’yan bindigar na ɗauke da makamai.

Umar, ya koka kan yadda ’yan bindiga ke yi wa manoma ɗauki ɗai-ɗai a yankin.

Amma, ya yaba da ƙoƙarin sojojin da aka tura yankin, sai dai ya roƙi gwamnati da ta aike da ƙarin jami’an tsaro masu yawa saboda yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a yankin.

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ba ta ce komai kan faruwar lamarin ba.

Jin ta bakin kakakin rundunar, ASP Mansir Hassan, ya ci tura domin ba ya amsa kiran waya.