✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe mutum 41 a Bakori

Mazaunan sun fita ne da nufin kwato dabbobinsu da ’yan bindigar suka sace.

Wasu ’yan bindiga sun kashe akalla mutum 41 da ake kyautata zaton ’yan kungiyar sa-kai ne a Karamar Hukumar Bakori ta Jihar Katsina.

Wadanda lamarin ya rutsa da su kamar yadda Aminiya ta samu rahoto, sun fita ne da nufin kwato dabbobinsu da ’yan bindigar suka sace.

Sai dai labari ya shan bamban yayin da ’yan bindigar suka yi wa jama’ar kwanton bauna wanda a dalilin haka mutum 41 daga cikinsu suka bakunci lahira sannan da dama suka jikkata.

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta bakin mai magana da yawunta, SP Gambo Isa ta ce, a ranar Laraba ce ’yan bindigar suka kai hari gidan wani Alhaji Muntari a Unguwar Audu Gare da ke kauyen Kandarawa a Karamar Hukumar ta Bakori.

SP Gambo ya ce ’yan bindigar sun yi awon gaba da dabbobi bayan harbe-harbe kan mai uwa da wabi domin razana mazauna kauyen.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, hakan ya janyo kungiyar ’yan sa-kan daga kauyuka 11 suka fita domin tunkurar ’yan bindigar a dajin ganin yadda tura ta kai bango.

Bayanai sun ce ’yan sa-kan sun yi kicibus ne da ’yan bindigar dajin ’Yargoje kuma babu wata-wata mutum 41 suka ce ga garinku nan.

Ya zuwa hada wannan rahoto, tuni an kwantar da wadanda suka jikkata a Babban Asibitin Kankara inda suke samun kulawa.