✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya dakatar da Shugabar NSIPA, Halima Shehu

Shugaba Tinubu ya maye gurbinta har zuwa lokacin da za a kammala bincike

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Shugabar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Kasa (NSIPA), Halima Shehu kan zargin almundahana.

Tinubu ya dakatar da ita ne a ranar Talata bayan zargin aikata zamba a hukumar sannan ya ba da umarnin za a gudanar cikakken bincike kan zargin da ake mata.

Shugaban kasar ya kuma da ba da umarnin maye gurbinta da Mista Akindele Egbuwalo a matsayin mukaddashin kodineta zuwa lokacin da za a kammala bincike.

Ya zuwa yanzu, shi ne mai kula da shirin na N-Power na kasa, kuma sabon nadin nasa zai fara aiki nan take.

Shugaba Tinubu ne ya nada Halima a watan Oktoban 2023, kuma Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin a ranar 18 ga watan Oktoba, 2023.