✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo

Shugaban ya kuma bai wa masu horas da tawagar kyautar dala dubu 50.

Shugaba Bola Tinubu ya karrama ’yan wasan tawagar ƙwallon ƙafa ta mata ta Nijeriya da lambar yabo ta OON.

Shugaban ya bai kowacce ’yar wasa a tawagar ta Super Falcons kyautar gida mai ɗakuna 3 a rukunin gidaje na Renewed Hope da kuɗi dala dubu 100—kwatancin naira miliyan 153.

Haka kuma, shugaban ya kuma bai wa masu horas da tawagar kyautar dala dubu 50.

A ranar Asabar ce Super Falcons ta Nijeriya ta lashe Gasar kofin ƙwallon ƙafa ta mata ta kasashen nahiyar Afirka a karo na 10, bayan samun nasara a kan mai masaukin baƙi Moroko da ci uku da biyu.