✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya naɗa Badaru Ministan Tsaron Najeriya

Ga cikakken jerin ma'aikatun da aka kowanne Minista

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu, ya nada tsohon Gwamnan Jihar Jigawa a matsayin sabon Ministan Tsaro na Najeriya.

Hakan dai na kunshe ne a cikin wata takarda daga Fadar Shugaban Kasar ranar Laraba da ke dauke da jerin ma’aikatun da shugaban ya ba Ministoci 45 din da Majalisar Dattijai ta sahale masa ya nada.

Shugaban ya kuma nada Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike a matsayin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, yayin da tsohon Gwamnan Filato, Simon Lalong ya zama Ministan Kwadago.

Ita kuwa Mariya Bunkure ta zama Ministar a Ma’aikatar Babban Birnin Tarayya, sai Atiku Bagudu da ya zama Ministan Kasafi da Tattalin Arziki.

Tahir Mamman – Ilimi

Yusuf Sununu – Karamin Ministan Ilimi

Nyesom Wike – Abuja

Mohammed Badaru – Tsaro

Bello Matawalle – Karamin Ministan Tsaro

Ahmed Dangiwa – Gidaje da Raya Birane

Abdullahi T. Gwarzo – Karamin Ministan Gidaje da Raya Birane

Simon Lalong – Kwadago da Ayyuka

Hannatu Musawa – Al’adu

Atiku Bagudu – Kasafi da Tsara Tattalin Arziki

Mariya Mahmud – Karamar Ministar Abuja

Bello Goronyo – Karamin Ministan Ruwa

Abubakar Kyari – Noma da samar da Abinci

Yusuf M. Tuggar – Harkokin Waje

Sa’idu A. Alkali – Harkokin Cikin Gida

Ali Pate – Lafiya

Ibrahim Geidam – Harkokin ‘Yan Sanda

Maigari Ahmadu – Karamin Ministan Karafa

Shu’aibu Abubakar Audu – Karamin Ministan Karafa

Mohammed Idris – Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a

Lateef Fagbemi – Shari’a/Babban Lauyan Gwamnati

Imaan Suleiman Ibrahim – Karamar Ministar ‘Yan Sanda

Zephaniah Jisalo – Ayyuka na Musamman

Joseph Utsev – Ruwa da Tsafta

Aliyu Sabi Abdullahi – Karamin Ministan Gona da Samar da Abinci

Bosun Tuani – Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani

Ishak Salaco – Karamin Ministan Muhalli

Wale Edun – Kudi da Tattalin Arziki

Bunmi Tunji – Ruwa

Adedayo Adelabu – Lantarki

Tunji Alausa – Karamin Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a

Dele Alake – Ma’adinai

Lola Ade-John- Yawon Bude Ido

Adegboyega Oyetola – Sufuri

Doris Anite – Masana’antu, Ciniki da Zuba Jari

Uche Nnaji – Kimiyya da Fasaha

Nkiruka Onyejeocha – Karamar Ministar Kwadago da Samar da Ayyukan Yi.

Uju Kennedy – Ministar Mata

David Umahi – Ayyuka

Festus Keyamo – Sufurin Jiragen Sama

Abubakar Momoh – Matasa

Betta Edu – Walwala da Yaki da Talauci

Ekperikpe Ekpo – Karamin Ministan Iskar Gas

Heineken Lokpobiri – Karamin Ministan Man Fetur

John Enoh – Wasanni

Majiyoyi daga Fadar Shugaban Kasa dai sun ce ba a kai ga sanya ranar rantsar da sababbin Ministocin ba, amma kwanan nan ake sa ran fara yi musu bita.