✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tankar ruwa ta take wasu kananan yara har lahira a Neja

Wata tankar dakon ruwa ta take wasu kananan yara mata biyu har lahira a unguwar Kwarkota da ke yankin Dutsen-Kura Gwari a Minna, Jihar Neja

Wata tankar dakon ruwa ta take wasu kananan yara mata biyu har lahira a unguwar Kwarkota da ke Dutsen-Kura Gwari a garin Minna, babban birnin Jihar Neja.

Kananan yaran sun gamu da ajalinsu ne a ranar Laraba a yayin da motar da ta kawo wa mazauna yankin ruwa take yin ribas, ta bi ta kansu bisa kuskure.

Aminiya ta gano cewa wani bawan Allah a unguwar ne ya dauki hayar tankin ruwan domin samar da ruwan sha kyauta ga mazauna yankin, bayan matsalar rashin ruwan sha da suke fama da ita ta kara tsanani.

Wani dan unugwar, Ahmed Isyaku, ya shaida wa wakilinmu cewa, “Mun jima muna fama da matsalar rashin ruwan sha a nan yankin.

“Shi ne wani bawan Allah ya dauki tankin ya kawo masa ruwa da mutanen unguwar, amma aka yi rashin sa’a, a lokacin da direban motar yake yin ribas, ya take wasu kananan yara mata, nan take rai ya yi halinsa.