✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojoji sun hallaka ’yan Boko Haram 5, wasu 44 sun miƙa wuya a Borno

Dakarun sun ce hare-haren da suke kai wa 'yan ta'addan ya sa wasu suka miƙa wuya.

Rundunar Sojin Najeriya, ta sanar da cewar dakarunta sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da kama wasu 44 da suka miƙa wuya a Jihar Borno. 

Wannan na ɗauke cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a shafinta na X (twitter), a ranar Talata.

A yayin ayyukansu, sojojin sun gano abubuwa masu fashewa, makamai, alburusai, da shanun da aka sace, sannan sun kama wasu masu laifi.

Sojojin, sun bayyana cewa a ranar Litinin, sun kai hari sansanin ’yan ta’addan ISWAP da ke yankin Bama a Jihar Borno.

A wannan samame, sun kashe ’yan ta’adda biyar tare da ƙwato wasu abubuwa kamar bam, RPG, bindigogi guda biyu, AK-47, alburusai 23, babura guda shida, da kuma wasu magunguna.

Kazalika, sojojin sun ce sakamakon ci gaba da kai hare-hare a yankin Arewa Maso Gabas, ’yan Boko Haram guda 44 da iyalansu sun miƙa wuya ga dakaru a yankunan Bama, Dikwa, da Gwoza na Jihar Borno.