✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sauya sheƙar Atiku ba sabon abu ba ne — Muƙaddashin Shugaban PDP

Shugaban ya ce sauya sheƙa ya zama ruwan dare a siyasa.

Muƙaddashin Shugaban Jam’iyyar PDP na Ƙasa, Iliya Damagum, ya ce ficewar Atiku Abubakar daga jam’iyyar ba abin mamaki ba ne.

Ya bayyana haka ne a ranar Juma’a, yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai a gidan gwamnati da ke Bauchi.

Damagum, ya ce irin wannan abu ruwan dare ne a siyasa, kuma yana da tabbacin cewa Atiku zai iya dawowa cikin jam’iyyar a nan gaba.

“Ba sabon abu ba ne, kuma ba zai zama na ƙarshe ba. Har yanzu muna sa ran zai dawo nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

Atiku Abubakar, wanda ya tsaya takarar shugabancin ƙasa a 2023 a jam’iyyar PDP, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar a ranar Laraba.

A cikin wata wasiƙa da ya aike wa shugaban mazaɓarsa da ke Jada, a Jihar Adamawa, ya ce ya fice ne saboda rikicin cikin gida da ke damun jam’iyyar.

Haka kuma, Atiku ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda jam’iyyar ke tafiya a yanzu, wanda ya ce ta kauce daga ainihin manufofi da aƙidun da aka kafa ta.