✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sabuwar yarjejeniyar tsagaita wuta za ta fara aiki a Sudan —MDD

Kazamin fada ya barke a babban birnin Sudan, Khartoum, a ranar 15 ga watan Afrilu.

Majalisar Dinkin Duniya ta yi maraba da yarjejeniyar tsagaita wuta da Amurka da Saudiyya suka jagoranta da ke shirin fara aiki, duk da cewa rikicin Sudan bai nuna wata alama ta ja baya ba.

Babban wakilin Majalisar Dinkin Duniya a Sudan, Volker Perthes ne ya shaida wa taron kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya hakan a ranar Litinin.

Ya bayyana cewa, “Wannan wani ci gaba ne na marhabin, ko da yake an ci gaba da gwabza fada da yunkurin sojoji har zuwa yanzu, duk da kudurin da bangarorin biyu suka yi na ba za su ci gaba da fada ba kafin tsagaita wutar ta fara aiki.”

Perthes ya ziyarci New York daga Port Sudan, ya ce MDD ta mayar da wasu ma’aikatanta da ayyukanta na wani dan lokaci zuwa birnin na Red Sea, bayan kazamin fada da ya barke a babban birnin kasar Khartoum, a ranar 15 ga watan Afrilu.

Yarjejeniyar tsagaita wuta mai dauke da sa hannun hafsan hafsoshin sojin kasar Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan, da kuma dakarun kungiyar sa kai karkashin jagorancin Janar Mohamed Dagalo, za ta fara aiki da karfe 9:45 na dare, lokacin yankin a ranar Litinin, kuma yana daukar tsawon kwanaki bakwai, wanda bangarorin za su iya sabunta ta.

Yayin da ake ci gaba da gwabza fada a lokacin tsagaita wuta da aka yi a baya, an amince da wannan a yayin gudanar da shawarwari a hukumance a birnin Jeddah na kasar Saudiyya, kuma zai hada da tsarin sanya ido da ya kunshi wakilai uku daga Saudiyya da Amurkawa da kuma sojojin Sudan biyu.