✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ruwan sama da iska sun lalata gidaje sama da 100 a Jigawa

Mazauna garin Kaugama na alhinin asarar gidaje da dukiyoyinsu sanadiyyar ruwan da iska.

Wata guguwa da ruwan sama mai ƙarfi sun yi ɓarna a Ƙaramar hukumar Kaugama da ke Jihar Jigawa, inda sama da gidaje 100 suka ruguje gami da asarar dukiya mai ɗimbin.

Tuni dai mazauna garin Kaugama suka alhinin asarar gidaje da dukiyoyinsu sanadiyyar mamakon ruwan mai haɗe da iska mai ƙarfi.

Musa Kaugama, wanda iftila’in ya rutsa da shi, ya ce gidansa mai ɗaki biyu ya ruguje, kuma ya yi asarar dukiyarsa.

“Na rasa komai sai ‘yan kayan da ba sa cikin ɗakunan,” in ji shi, yana mai roƙon hukumomi da su taimaka.

Ali Haruna Kaugama, wani mazaunin unguwar da abin ya shafa, ya bayyana cewa ɗakinsa mai ɗaki uku ya lalace sosai.

“Gini na yana tsaye, amma duk rufin da aka yi ya tafi,” in ji shi.

Garba Musa Yalo Kaugama, mazaunin Unguwar Gabas, ya ruwaito cewa gidansa mai ɗaki biyu ya lalace gaba ɗaya, kuma duk kayansa sun lalace.

Dokta Haruna Mairiga, Babban Sakataren Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), ya ce an aike da tawagar da za ta tantance irin ɓarnar da aka yi tare da bayar da tallafi ga waɗanda abin ya shafa.

“Ba za mu tsaya ba tare da taimaka wa waɗanda abin ya shafa ba,” in ji shi.

Ya kuma ƙara da cewa wasu yankunan jihar da suka haɗa da Fagam da ke Ƙaramar Hukumar Gwaram da kuma wasu sassan Ƙaramar Hukumar Ringim su ma abin ya shafe su.