✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rufe kan iyakokin Najeriya: Buhari ya ce kwalliya ta biya kudin sabulu

Ya ce yana sane ya sa aka kulle boda

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce yanzu mutane na ganin amfanin hikimarsa ta kulle iyakokin kasar.

Ya bayyana hakan ne a ranar Talata, lokacin da yake jawabi a yayin bude sabuwar hedkwatar Hukumar Kwastam ta Kasa a Abuja.

An gina sabuwar hedkwatar ce a kan Naira biliyan 19.

A cewar Buhari irin wadancan manufofin na rufe iyakoki, za a jima ana cin moriyarsu, saboda kwalliya ta biya kudin sabulunsu.

Buhari, ya kuma ce hana shigo da shinkafa ’yar kasar waje na daya daga cikin irin makamantan matakan.

“Da gangan na rufe iyakokin tsandauri. Na ce ko dai kowa ya ci abin da muke nomawa, ko kuma mu noma abin da za mu ci. Daga bisani kuma mutane sun ga amfanin haka,” in ji Buhari.