✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rikicin Pakistan: An kama kusoshin jam’iyyar Imran Khan

Gwamnati ta tura sojoji don murkushe tarzomar da ta barke sakamakon kama Khan kwanaki uku da suka gabata

Gwamnatin Pakistan sun kama wani babban jigo na jam’iyyar tsohon Firayim Minista Imran Khan a ranar Alhamis, a yayin da gwamnati ta tura sojoji don murkushe tarzomar da ta barke sakamakon kama Khan kwanaki uku da suka gabata.

A cikin dare ne dai jami’an tsaron suka kama Shah Mahmood Qureshi, wanda ya kasance Ministan Harkokin Waje na shekara hudu a lokacin da Imran Khan ke firayim minista.

An kuma kama wasu manyan jiga-jigai biyu na jam’iyyar PTI ta Mista Khan —  Asad Umar da Fawad Chaudhry a ranar Laraba.

Kawo yanzu an kashe akalla mutum biyar bayan da tarzomar da ta biyo bayan kama Mista Khan da hukumar yaki da rashawa ta kasar ta yi a ranar Talata ta kara munana.

Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da Pakistan ke a kasar mai mutane miliyan 220 ke fama da matsananciyar matsalar tattalin arziki da kuma jinkirin samun dauki daga Asusun ba da Lamuni na Duniya (IMF) tun watan Nuwamba.

Masu zanga-zangar sun kutsa kai cikin gine-ginen sojoji tare da kai farmaki gidan wani babban hafsan soji a birnin Lahore da ke gabashin kasar; sun kuma kai hari tare da kona wasu gine-gine da kadarorin gwamnati.

A ranar Laraba gwamnatin kasar ta amince da bukatar gwamnatin birnin Islamadan da kuma biyu daga cikin larduna hudu na kasar — Punjab da Khyber Pakhtunkhwa, wadanda kowacce daga cikinsu tungar Khan ce, — na tura sojoji domin dawo da zaman lafiya.

Rundunar ’yan sandan Islamabad ta fada a safiyar ranar Alhamis cewa sojoji sun isa babban birnin kasar.

’Yan sanda dai sun kama masu zanga-zanga sama da 1,300 a lardin Khan na Punjab saboda tashin hankali.