✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rashin wajen sauka a filin jirgin Katsina ne ya hana ni zuwa jana’izar Buhari – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce rashin samun wurin da jirginsa zai sauka ne a filin jirgin sama na Katsina ya sa bai samu…

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce rashin samun wurin da jirginsa zai sauka ne a filin jirgin sama na Katsina ya sa bai samu halartar jana’izar tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ba.

A ranar Talata ce dai aka binne Buhari a gidansa da ke Daura a jihar Katsina bayan rasuwarsa a asibiti a Landan ranar Lahadi, yana da shekara 82.

To sai dai Akpabio ya ce duk ƙoƙarin direban jirginsu na samin wurin yin fakin ya ci tura, tilas suka koma Abuja.

A wani saƙo da Akpabio ya wallafa a shafinsa na Facebook ranar Laraba, ya ce, “Jiya, direban jirginmu ya yi ta ƙoƙarin sauka a filin jiragin sama na Katsina, amma saboda cunkoson jirage da rashin wurin fakin, dole muka hakura muka koma Abuja. Abin da ya hana a gan ni a wajen jana’izar Buhari ke nan.

“Amma yau [Laraba], na sami rakiyar abokaina Sanatoci inda muka ziyarci iyalan Buhari a gidansa na Daura, muka yi musu ta’aziyya.

“Mun kuma yi masa addu’ar neman gafarar Allah sannan mun jajanta wa matarsa da ’ya’yansa da sauran ’yan uwansa,” in ji Akpabio.

Shugaban majalisar ya kuma ce daga nan sun ziyarci Sarki Daura, Alhaji Umar Farouk Umar domin ya masa ta’aziyya.

Ya ce sun kuma ce sun ziyarci Gwamnan Katsina, Dikko Umar Radda, inda shi ma suka yi masa ta’aziyyar.