✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NAJERIYA A YAU: ‘Karambanin’ Malamai kan ƙudurorin Harajin Tinubu

Shin karambani ne ya sa malamai tsoma baki a muhawarar ƙudurorin Harajin Tinubu ko neman maslaha ga al’umma?

More Podcasts

Kudurorin Dokar Haraji da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike wa Majalisar Dokoki ta Ƙasa suna ci gaba da tayar da kura a Najeriya.

Muhawara a kan batun ta dauki sabon salo ne bayan da wasu malaman addinin Musulunci daga Arewacin Najeriya suka ki amincewa da wasu tanade-tanaden ƙudurorin dokar.

Shin har da su kaza ne a cin danko? Karambani ne ya sa malamai tsoma baki a muhawarar ko neman maslaha ga al’umma? A kan waɗannan batutuwa shirin Najeriya A Yau zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan