✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 15 sun mutu bayan jiragen kasa sun yi karo a Indiya

Lamarin ne na baya-bayan nan da ya afku a layin dogo na Indiya, wanda ke daukar miliyoyin fasinjoji a kowace rana.

Kimanin mutane 15 sun mutu wasu da dama sun jikkata bayan wani jirgin kasa mai daukar kaya ya yi taho-mu-gama da wani na fasinja a kasar Indiya.

A safiyar Litinin ne jirgin dakon kaya ya yi taho-mu-gama da jirgin fasinjan kamfanin Kanchanjunga Express a gundumar Darjeeling da ke Jihar Bengal ta Yamma.

Wani babban jami’in ’yan sanda a gundumar Darjeeling, Abhishek Roy, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, an zakulo gawarwaki sama da 15 daga cikin jiragen kasan.

Roy ya kara da cewa, kusan mutane 30 ne suka jikkata, amma masu aikin ceto da likitoci  suna ci gaba da aiki a yayin da mazauna yankin da jami’an agaji ke kokarin kawar da tarkacen jiragen kasan da abin ya shafa.

Kakakin hukumar jiragen kasa a yankin arewa maso gabashin kasar, Sabyasachi De, ya ce uku daga cikin wadanda suka mutu ma’aikatan jirgin kasa ne.

Babban Ministan West Bengal, Mamata Banerjee, ya ce, an tura likitoci, motocin daukar marasa lafiya da jami’an agaji zuwa wurin da hadarin ya afku, wanda ke kusa kusa da tashar New Jalpaiguri.

Rahotannin farko dai sun nuna cewa kuskuren dan Adam ne ya haddasa hatsarin jiragen kasan.

Layukan dogon kasar Indiya da ke yawan jigilar jama’a suna yawan samun haddura a kowace shekara.