✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Muna samun sauki bayan hatsarin mota — Gwamna Radda

Gwamnan Jihar Katsina ya bayyana hakikanin halin da yake ciki bayan hatsarin motar da shi da abokan rakiyarsa suka yi a hanyar Daura zuwa Katsina.

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya magantu, inda ya bayyana hakikanin halin da yake ciki bayan hatsarin motar da shi da abokan rakiyarsa suka yi a hanyar Daura zuwa Katsina.

A cikin wani sakon bidiyo da gwamnan ya yi daga asibiti, ya bayyana cewa shi da abokan tafiyar tasa da hatsarin ya ritsa da su suna samun sauki.

Ya bayyana cewa, “Allah Ya jarabce mu da hadarin mota, amma mun samu sauki, Alhamdulillahi.

“Muna nan ana ci gaba da duba mu [a asibiti] domin kara samun sauki. Muna kuma godiya da addu’o’in da ake mana.”

Aminiya ta ruwaito cewa wata mota kirar Golf ce ta kwace ta tsallaka hannun da motar gwamnan take, inda suka yi taho-mu-gama.

Babban Sakataren Yaɗa Labaran gwamnan, Ibrahim Muhammad Kaula ya bayyana cewa wani ɗan Majalisar Tarayya da ke tare da Gwamna Raɗɗa a lokacin ya samu karaya a hatsarin.

Ya ƙara da cewa Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, Abdulƙadir Mamman Nasir, ma ya samu raunuka a hatsarin amma gwamnan bai samu wasu raunuka masu tsanani ba.

Rahotanni sun bayyana cewa duk mutanen da ke cikin karamar motar sun samu karaya.