✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Matatar man Dangote za ta fara aiki nan da mako 2

Buhari zai kaddamar da matatar mako guda kafin saukarsa daga mulki

Nan da mako biyu masu zuwa katafariyar matatar mai ta Dangote mai karfin samar da ganga dubu 650 na tataccen mai a kullum za ta fara aiki.

Babban Jami’in Hulda da Jama’a na Rukunin Masana’antun Dangote, Anthony Chiejina, ya sanar a ranar Lahadi cewa za a kaddamar da sabuwar matatar ne ranar 22 ga watan Mayu da muke ciki.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ne zai a kaddamar da matatar man a Legas, mako guda kafin saukarsa daga mulki.

Gwamnatin Tarayya na sa ran fara aikin sabuwar matatar, wadda kamfanin mai na kasa (NNPCL) ke da hannun jari a ciki, zai taimaka wajen magance matsalar mai da ake fama da ita a Najeriya.

Sabuwar masana’antar ta Dangote za ta kuma rika samar sauran dangogin man fetur daga danyen mai da take tacewa.

Matatar, wadda aka gina a kan kudi Dala biliyan, ita ce mafi girma a daukacin nahiyar Afirka, kuma ta zarce da dama daga cikin manyan masan’antun mai na duniya.