✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masamar Wutar Lantarkin Najeriya Ta Durkushe A Karo Na 6 A 2024

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki ta Najeriya ya tabbatar da dukushewar masamar wutar lantarkin kasar a karo na shida cikin watanni hudu a bana

Cibiyar samar da wutar lantarki ta Najeriya ta durkushe a karo na shida cikin watanni hudu a shekarar 2024.

Aminiya ta ruwaito cewa cibiyar samar da lantarkin ta durkushe ne da misalin karfe 2:42 na dare, kafin wayewar garin ranar Litinin.

Durkushewar ta sa karfin wutar lantarkin kasar ya ragu zuwa megawatt 64.70.

Hukumar kula samar wa lantarki ISO mai zaman kanta na nuni da cewa a halin yanzu tashar tana samar da wutar lantarki mai karfin 266.50mw daga tashoshin Okpai da Geregu da kuma Ibom.

Wata sanarwa daga kamfanin rarraba wutar lantarki a Filato ta tabbatar da cewa “Katsewar da ake fuskanta a halin yanzu a Najeriya ta samo asali ne sakamakon raguwar karifn wutar lantarki daga cibiyar samarwa ta kasa da misalin karfe 02:42am na ranar Litinin 15 ga Afrilu, 2024”.

Sanarwar da shugaban sashen kula da harkokin kamfanoni, Dakta Friday Adakole Elijah, ya fitar, ta ce kamfani na sa ran a gyara matsotsar domin samar da wutar lantarki ga abokan hulda.