✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Magoya bayan NNPP sun yi zanga-zanga kan hukuncin kotu a Kano

Mutanen dai na neman kotun daukaka kara ta yi wa Abba adalci

Wasu magoya bayan jam’iyyar NNPP sun fantsama a kan titunan birnin Kano suna zanga-zangar neman kotun daukaka kara ta yi wa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, adalci.

Mutanen dai sun yi zanga-zangar ce da yammacin Laraba don su nuna bacin ransu kan ce-ce-ku-cen da suka ce hukuncin kotun na ranar Juma’a ya janyo sakamakon tufka da warwarar da suka ce yana cike da shi.

Mutanen dai sun halarci wata sallah ta musamman ne a filin Mahaha da ke Ƙofar Na’isa a birnin na Kano wajen misalin ƙarfe 2:00, daga bisani sun fantsama tituna suna neman a yi wa jam’iyyarsu da ɗan takararta adalci.

Hakan na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan bayyanar kundin hukuncin kotun na ainihi da a wasu shafukansa ya nuna kotun ta jingine hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben da ya dakatar da Abba sannan ya ayyana Nasir Yusuf Gawuna na APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

Ga wasu daga cikin hotunan zanga-zangar: