✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda Jiragen Sojin Najeriya Suka kashe Fararen Hula 400 Bisa Kuskure

Jiragen sojin Najeriya sun kashe farare hula sama da 400 daga 2014, a bisa kuskure.

Fararen hula sama da 400 jiragen sojin Najeriya suka kashe a bisa kuskure a kasar daga shekarar 2014 zuwa yanzu.

Harin da wani jirgi mara matuki ya kai wa masu taron Mauludi a Jihar Kaduna ranar Lahadi shi ne na 16 kuma mafi muni, inda aka rasa kimanin mutun 90.

Na biye da shi, shi ne wanda aka rasa rayuka 60 a Zamfara, sai na uku wanda aka rasa wasu 58 a Borno.

Sau shida irin haka na faruwa a Jihar Borno.

Ga jerin lokutan da irin haka ta faru da kuma yawan fararen hula da aka yi asara:

  1. Mutum 10 a Jihar Borno a harin ranar 16 ga watan Maris, 2014.
  2. Mutum 58 a Borno 17 ga watan Janairun 2017
  3. Mutum 20 a 28 ga watan Fabrairun 2018
  4. Mutum 11 a Zamfara ranar 11 ga Afrilun 2019
  5.  Mutum 13 a ranar 2 ga Yulin 2019
  6. Mutum 30 a Borno ranar 25 ga Afrilun 2021.
  7. Mutum 9 a Yobe a ranar 26 ga watan Satumbar 2021
  8. Mutum 20 a Borno a ranar 26 ga watan Satumbar 2021.
  9. Mutum 6 a Neja a ranar 20 ga watan Afrilun 2022.
  10. Mutum 12 a Katsina a ranar 6 ga watan Yulin 2022.
  11. Mutum 60 a Zamfara a ranar 17 ga watan Disambar 2022.
  12. Mutum 18 a Neja a ranar 24 ga watan Janairu 2023.
  13. Mutum 40 a Nassarawa ranar 25 ga Janairu
  14.  Mutum 3 a Kaduna a ranar 5 ga watan Maris sin 2023
  15. Mutum 1 a Neja a ranar 18 ga Agustan 2023.
  16. Mutum 90+ a Kaduna a ranar 3 ga Dismabar 2023.