Hukumar Kwallon Kafa ta Ingila (FA) ta fitar da jadawalin wasan kusa da na karshe (Semi Fainal) na gasar cin Kofin Carabao da aka fi sani da Kofin Carling.
Jadawalin ya nuna kulob din Manchester United zai kara da Manchester City a ranar Talata 6 ga Janairu mai zuwa, yayin da ranar Laraba 8 ga Janairu 2020 kulob din Leicester City zai kece raini ne da na Aston Billa.
Sai wasanni karo na biyu za a yi su ne a ranakun Talata 28 ga Janairu a tsakanin Aston Billa da Leicester City yayin da a ranar Laraba 29 ga Janairu za a hadu a tsakanin Manchester City da Manchester United, inda kungiyoyi biyu da suka samu nasara a wasannin biyu za su haye wasan karshe wato fainal.
Kulob din Manchester City ne ya lashe kofin sau biyu a jere inda yake hankoron lashe na uku a wannan karo.