✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kebbi ta rasa mahajjaci na uku a Saudiyya

Mutum na uku a cikin maniyyatan Jihar Kebbi ya rasu kwanaki uku kafin fara aikin Hajji a kasar Saudiyya.

Mutum na uku a cikin maniyyatan Jihar Kebbi ya rasu kwanaki uku kafin fara aikin Hajji a kasar Saudiyya.

Hukumar kula da jin dadin alhazan jihar ta sanar cewa mahajjacin mai suna Alhaji Abubakar Abdullahi ya rasu ne a birnin Makkah sakamakon gajeruwar rashin lafiya.

Shugaban hukumar, Alhaji Farouk Aliyu-Enabo, ya sanar da cewa marigayi Alhaji Abubakar Abdullahi dan yankin Gulma ne daga Karamar Hukumar Argungu ta Jihar Kebbi.

Sanarwar ta kara da bayyana cewa an yi wa marigayin jana’iza a Masallacin Harami kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Ya kuma mika sakon ta’aziyyar hukumar da gwamnatin jihar ga iyalan mamatan tare da rika musu rahamar Allah.

A halin da ake ciki, hukumomin aikin Hajji sun shawarci maniyyata da su dauki matakan kariya musamman saboda yanayin tsananin zafin rana da ake ciki a Saudiyya a halin yanzu.

Hukumomin aikin Hajji na kasa da na jihohin Najeriya na ci gaba da gudanar da cibiyoyin kuka da lafiyar alhazansu a biranen Makkah da Madina.