✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kano Pillars ta aika wa Ahmed Musa sakon taya murna

kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars wanda ake yi wa lakabi da “Sai Masu Gida” ta aika wa tsohon dan kwallonta da yanzu haka yake…

kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars wanda ake yi wa lakabi da “Sai Masu Gida” ta aika wa tsohon dan kwallonta da yanzu haka yake bugawa kulob din CSKA Mosco da ke Rasha kwallo sakon taya murna bayan kocin kungiyar kwallon kafa ta Super Eagles Sunday Oliseh ya zabe shi a matsayin kyaftin din kungiyar a makon jiya.
A wata sanarwa da kulob din ya fitar dauke da sanya hannun jami’in hulda da jama’a Rilwanu Idris Malikawa ya bayyana nadin a matsayin abin da ya dace, inda kulob din na Pillars ya yi masa fatan samun nasara.
Ahmed Musa dai ya taba yi wa kulob din Kano Pillars kwallo kafin ya samu nasarar haurawa kasar waje.  Yana daga cikin ’yan kwallon da suka taimakawa Pillars wajen yin fice a ciki da kuma wajen kasa.
Koci Sunday Oliseh ya ba shi mukamin kyaftin a kungiyar Super Eagles ce bayan ya samu sabani da tsohon kyaftin din kuma golan kungiyar bincent Enyeama a makon jiya, inda daga bisani Enyeama ya bayar da sanarwar yin ritaya daga yi wa kungiyar kwallo.
Tuni masu sha’awar kwallo suka rika yin muhawara a kan dalilin yin ritayar Enyeama daga kungiyar da kuma mayar da Ahmed Musa kyaftin din kungiyar.