✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna

Aisha ta koma gidan marigayin ne bayan shafe kwanaki tana karɓar gaisuwa a Daura.

Aisha ta koma gidan mijinta, marigayi Muhammadu Buhari da ke Jihar Kaduna, bayan shafe kwanaki a Daura tana karɓar gaisuwa.

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, ce ta jagoranci tawagar gwamnatin jihar wajen tarbar Aisha a Filin Jirgin Sama na Kaduna a ranar Lahadi.

Daga cikin waɗanda suka tarbe ta akwai Shugabar Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, Munira Suleiman Tanimu, da wasu manyan jami’an gwamnati.

Tarbar da aka yi mata ta nuna yadda jihar ke ci gaba da girmama tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari da iyalinsa bisa gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban ƙasar nan.

Bayan tarbar ta, Dakta Hadiza ta raka Aisha Buhari da iyalanta zuwa gidan marigayin.

Wannan ya nunacewar iyalan marigayin za su ci gaba da rayuwa a jihar, tare da ƙarfafa zumunci tsakanin gwamnatin jihar.

Dubban mutane na ci gaba da miƙa ta’aziyyarsu kan rasuwar tsohon shugaban wanda ya mulki Najeriya sau biyu.

 

Ga hotunan a ƙasa: