✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

HOTUNA: Wike ya gana da Abure yayin da rikicin LP ke ƙara ƙamari

An jima ana zargin Abure da yi wa jam'iyyar LP zagon ƙasa, amma ya musanta dukkanin zarge-zargen.

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya karɓi baƙuncin Julius Abure, ɗaya daga cikin shugabannin jam’iyyar LP, a gidansa da ke Abuja.

Zuwa yanzu dai ba a san dalilin wannan ganawa ba, amma mutane da dama sun fara surutu da hasashen abin da shugabannin suka tattauna.

Wike wanda yake ɗan jam’iyyar PDP, amma a yanzu yana aiki a Gwamnatin jam’iyyar APC.

An zargi Julius Abure da yi wa jam’iyyarsa ta LP zagon ƙasa, amma ya musanta waɗannan zarge-zarge.

Lere Olayinka, mai magana da yawun Wike, ne ya yaɗa hotunan wannan ganawa a ranar Lahadi.

Ga hotunan ganawar a ƙasa: