✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci

A yau din aka samu rahoton ganin watan sabuwar shekarar musulunci ta 1447 Bayan Hijira a Saudiyya.

Gwamnatin Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga watan Yunin 2025, a matsayin hutun rana daya na sabuwar shekarar musulunci ta 1447.

Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da ofishin shugaban ma’aikatan Kano ya fitar a yammacin wannan Larabar.

Sanarwar wadda babban sakatare a ofishin shugaban ma’aikatan, Ashiru Abdullahi ya fitar, ta bukaci ma’aikatan jihar da su yi amfani da wannan dama domin yi wa jihar da kuma kasa baki ɗaya addu’ar zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.

Aminiya ta ruwaito Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, a jiya Talata yana ba da umarnin fara duban watan Muharram na sabuwar shekarar musulunci ta 1447 daga yau Laraba, 29 ga watan Zulhijjan 1446.

Kawo yanzu Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Islama da Sarkin Musulmin ke jagoranta ba ta sanar da ganin jinjirin watan na Muharram ba.

Sai dai kuma a yau din aka samu rahoton ganin watan sabuwar shekarar musulunci ta 1447 Bayan Hijira a Saudiyya.

Cikin wani saƙo da shafin Haramain na Saudiyya ya wallafa ya ce an ga watan da maraicen yau Laraba, 25 ga watan Yuni.

Hakan na nufin shekarar 1446 ta zo ƙarshe wannan rana a ƙasar ta Saudiyya, inda goben za ta kasance 1 ga Muharamm, watan farko a kalandar musulunci.