✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ghana ta doke Koriya ta Kudu a Gasar Kofin Duniya

Yanzu haka Ghana na da maki 3 a teburi, a matsayi na biyu.

Ghana ta samu nasarar doke Koriya ta Kudu a ci gaba da wasannin Gasar Kofin Duniya da ke gudana a kasar Qatar.

Wannan gagarumar nasarar ta farfado da damar da Ghana ke da ita ta zuwa zagaye na gaba, muddin kasar ta samu nasara a wasanta na karshe da za ta fafata da Uruguay.

Mohammed Salisu ya fara jefawa Ghana kwallo a wasan, yayin da Mohammed Kudus ya jefa ta biyu a zagaye na farko.

Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Koriya ta Kudu ta farke ci biyun ta hannun dan wasanta Cho Gue-sung, abin da ya jefa fargaba tsakanin magoya bayan kasar Ghana.

A minti na 68 Mohammed Kudus ya jefa kwallo ta 3, abin da ya bai wa Ghana nasara, duk da yake ‘yan kasar Koriya ba su yi kasa a gwiwa ba, sakamakon munanan hare-haren da suka yi ta kaiwa har zuwa lokacin tashi a wasan.

Yanzu haka Ghana na da maki 3 a teburi, a matsayi na biyu, yayin da Portugal ke sahun gaba da maki 3, kafin karawar da za ta yi da Uruguay a yammacin ranar Litinin.

Ganin irin wadannan munanan hare-hare, hankalin magoya bayan Ghana ya tashi, musamman yadda alkalin wasa ya kara mintina 10 kafin ya tashi wasan.