Burkina Faso ta doke Najeriya 3-1 a kwallon kafa
Kamaru ta yi wa Falcons kancal da ci 2-1
kungiyiyon wasan kwallon kafa na maza da mata da suka wakiltar Najeriya a Gasar Wasanni ta Afirka sun gaza kaiwa wasan karshe na neman lambar zinare a wasannin da ake fafatawa a kasar Kongo.
kungiyar kwallon kafa ta matasa ’yan kasa da shekara 23 da ake wa kirari da The Dream Team bI ta sha kashi a hannun takwararta ta kasar Burkina Faso da ci 3-1, yayin da kasar Kamaru ta doke Najeriya a bangaren kwallon mata da ci 2-1 a wasan da aka fafata ranar Talata.
Doke kungiyoyin biyu ya ba ’yan wasan mamaki wadanda suka rika kurin cewa sun je wasan ne da niyyar dawowa da lambar zinare daga kasar Kongo.
Kocin kungiyar Najeriya a gasar, Samson Siasia ya yi canje-canje biyu ga jerin ’yan wasansa na farko kafin fafatawa da Burkina Faso, inda ya kawo Femi Oladapo a madadin dan wasan nan mai hazaka Daniel Etor, kuma ya fifita Christian Pyagbara kan ya fara wasa a zubin farko maimakon Kinglsey Sokari.
Bayan samun tikitin zuwa wasan kusa da na karshe a matsayin zakarun rukunin B ’yan wasan Najeriya sun sakankance ’yan wasan Young Stallions ba za su iya dakile su daga cimma burinsu ba, kafin reshe ya juye da mujiya.
kwallayen da suka fito daga mai tsaron baya Seth Sincere da Omar Kabore da kuma Arba Dicko ne suka ba Burkina Faso nasara a kan Najeriya, wadda ta sa rai ta sake cin lambar zinare a karo na biyu a wannan gasa da ta taba lashe lambar zinare a wasan da aka yi a Najeriya a 1973.
Da wannan sakamako kasar Burkina Faso ta kai wasan karshe, inda za ta kara da kasar Senegal, wadda ta kai wasan karshe bayan da ta doke kasar Kongo da ci 3-1.
kungiyar kwallon kafa ta ’yan mata wato Falcons, wadda ta fara wasa da ban sha’awa ta hanyar doke kasashen Kongo da Tanzaniya, ta gaza cin was anta na karshe a rukuninsu inda Kwaddibuwa ta doke ta, kafin yanzu ta sake mika wuya ga kasar Kamaru, wadda ta kai wasan karshe bayan da ta doke ’yan matan Najeriya da ci 2-1.
Kamaru za ta fafata a wasan karshe ne da kasar Ghana wacce ta samu nasara a kan Kwaddibuwa da ci daya mai ban haushi.
Yanzu dai abin da ya rage wa kungiyoyin biyu na Najeriya, wato Dream Team bI da Falcons shi ne su wanke kansu ta hanyar lashe lambobin azurfa ku su dawo gida hannu rabbana.