Duk da rashin zura kwallo a raga a gasar cin kofin duniya da ke gudana a halin yanzu a Brazil, dan wasan gaban Najeriya Emmanuel Emenike zai canza sheka daga kulob dinsa Fenerbahce da ke Turkiyya zuwa na Chelsea a Ingila kafin a fara kakar wasa ta bana. Kakar wasa ta bana za ta fara ne a watan gobe (Agusta) idan Allah Ya kaimu.
Kafar sadarwar Dailymail ta Ingila ce ta kalato wannan labari a shekaranjiya Laraba. Ta ce tuni kulob din biyu suka cimma matsaya a kan canjin sheakar dan kwallon. An ruwaito cewa kulob din Chelsea ya amince ya bai wa kulob din Fenerbahce zunzurutun Yuro miliyan 19 kwatankwacin Naira biliyan 4 da miliyan 300 don canza shekar dan kwallon.
Emenike dai ya zura kwallaye 12 daga cikin wasanni 28 da ya yi a gasar rukuni-rukuni na Turkiyya a kakar wasan da ta wuce.
Yana daga cikin ’yan kwallon da suka wakilci Najeriya a gasar cin kofin duniya da ke gudana a halin yanzu kuma Faransa ce ta fitar da Najeriya da ci 2-0 a ranar Litinin da ta wuce.
Emenike zai koma Chelsea
Duk da rashin zura kwallo a raga a gasar cin kofin duniya da ke gudana a halin yanzu a Brazil, dan wasan gaban Najeriya Emmanuel…