✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

De Bruyne ya sake lashe gwarzon dan wasan Firimiya

Dan wasan ya sake lashe kyautar gwarzon dan wasa a karo na biyu a jere.

Fitaccen dan wasan tsakiya na kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Kevin De Bruyne, ya sake lashe kyautar gwarzon dan wasan gasar Firimiyar Ingila a karo na biyu.

Dan wasan mai shekara 29, ya kafa tarihi wajen lashe kyautar  kungiyar kwararrun ’yan wasan Ingila ajin mazaa karo na biyu a jere kwatankwacin tarihin da Cristiano Ronaldo ya kafa a lokacin da yake Manchester United.

  1. An sace Hakimi da matansa biyu a Neja
  2. Ya kamata jihohin Arewa su sake fasalin nomansu — Sa’ad Gulma

De Bruyne wanda dan asalin kasar Belgium ne, ya zura kwallaye shida a bana tare da taimakawa wajen zura kwallaye 12 a raga.

Dan wasan ya taka muhimmiyar rawa inda taimaka wa kungiyarsa ta Manchester City wajen lashe gasar Firimiyar Ingila a bana.

Sai dai kungiyar tasa ta yi rashin nasara a hannun Chelsea ta ci daya mai ban haushi a wasan karshe na gasar cin Kofin Zakarun Turai.