✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

COVID-19: Saudiyya ta sake bude tashoshin jirage

Saudiyya a kuma bude iyakokinta bisa wasu sharudda da ta shimfida

A yammacin Asabar ne Ma’aikatar Cikin Gida ta Saudiyya, ta ba da umarnin sake bude filayen jiragen kasar, iyakokin kasa da na ruwa.

A ranar 20 ga Disambar 2020 ne Saudiyya ta rufe iyakokinta da kuma filayen jiragen sama, saboda sake bullar cutar cutar coronavirus a wasu kasashen Turai.

Dokar bude filin jirgin saman da iyakokin ta fara aiki ne a ranar Lahadi 3 ga Janairu 2021 bisa wasu sharuda da aka gindaya:

Duk bakon da zai shiga kasar daga kasar Birtaniya ko Afrika ta Kudu, to zai killace kansa na tsawon kwana 14.

Duk dan kasar da ya dawo daga tafiya, shi ma dole ya killace kansa a gida har tsawon mako biyu, sannan za a rika bincikar lafiyarsa a-kai-a-kai.

Matafiya daga kasashen da cutar ta sake bulla kuma dole ne su ma su killace kansu na kwana 7, za kum a yi musu gwajin cutar.

Matafiya da suka shigo kasar daga kasashen da cutar ba ta sake bulla ba kuma, za su killace kansu na tsawon kwana 3 kuma za a yi musu gwajin cutar.