✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Chelsea ta nada Lampard kocin wucin gadi

Lampard ya sake dawowa Chelsea a karo na biyu.

Kungiyar Kwallon Kafa ta Chelsea ta nada tsohon dan wasanta, Frank Lampard a matsayin mai horaswa na wucin gadi.

Karo na biyu ke nan da Lampard ya zama kocin Chelsea, bayan sallamar sa da kungiyar ta yi a 2021.

Ta nada Thomas Tuchel a matsayin wanda ya maye gurbinsa, amma kwalliya ta gaza biyan kudin sabulu a farkon kakar wasanni ta 2023.

Chelsea ta sallami Tuchel daga aiki ta kuma nada Graham Potter a matsayin sabon kocinta.

Shi ma Potter ta sallame shi a satin da ya wuce bayan gaza yin katabus a wasanni 32 da ya jagoranci kungiyar.

Lampard, ya kasance a zaune babu aiki tun a watan Janairu da kungiyar kwallon kafa ta Everton ta sallame shi daga aiki.

Wasanni tara ne suka rage wa Chelsea a gasar Firimiyar Ingila, inda take a matsayi na 11 a teburin gasar.

A sati mai zuwa kungiyar za ta barje gumi da Real Madrid a Gasar Zakarun Turai.