✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi wa ’yar jaridar Najeriya, Toke Makinwa fashi a London

Makinwa ta bayyana kaduwarta da fashin da aka yi mata a birnin London na kasar Birtaniya

Fitacciyar ’yar jaridar nan, Toke Makinwa, ta ce ’yan fashi sun raba ta da wasu muhimman kayayyakinta a birnin London.

Makinwa, mai gabatar da shirye-shirye a rediyo da talabijin da ta sanar da fashin da aka yi mata ne ta shafinta na ‘Snapchat’.

Ta ce, “Yanzu aka yi mini fashi a London, na ma rasa abin cewa. Ta yaya hakan za ta faru da ni?” inji ta.

Wasu ra’ayoin da aka bayyana a karkashin sakon da Toke Makinwa ta wallafa sun nuna London  da Legas tamkar wa da kani ne inda ake fama da bata-gari, kuma akwai ’yan Najeriya mazauna birnin da daman gaske.

Idan za a iya tunawa, kwanan nan gwamnatin Najeriya ta shawarci ’yan aksar masu shirin zuwa Amurka da Birtaniya da wasu kasashen Turai da su yi hattara da barayi a can.