✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An sace tsohon Sakataren Gwamnati a Inugu

Maharan sun tazama mutane da harbi kafin sace tsohon sakataren gwamnatin

’Yan bindiga sun sace tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Inugu, Dokta Dan Shere, tare da wasu matafiya da ba a tantace adadinsu ba.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis a hayar Enugu zuwa Ugwuogo, Nike zuwa Nsukka, a lokacin da Shere ke kan hanyarsa ta dawowa daga wani taro da ya halarta.

Majiyarmu ta ce ’yan bindigar wanda adadinsu ya kai takwas, sai da suka yi harbe-harben bindiga a iska don razana jama’a kafin daga bisani suka yi garkuwa da su.

Sace mutanen ya jefa jama’ar yankin cikin mummunan tashin hankali, inda suka yi kira ga jami’an tsaro da a gaggauta daukar matakin ceto su.

Shere ya yi Sakataren Gwmanatin jiahr ne a zamanin tsohon Gwamnan Inugu, Chimaroke Nnamani.