✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kashe ’yan bindiga 4, an kama wasu 13 a Kaduna

'Yan sandan sun samu nasarar ne biyo bayan bayanan sirri da suka samu.

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna, ta kashe wasu mutane hudu da ake zargi da garkuwa da mutane tare da cafke wasu 13 a wani samame da ta kai a sassan jihar.

Da yake bayyana hakan a lokacin da yake gabatar da wadanda ake zargin, mukaddashin kakakin rundunar, ASP Manir Hassan, ya shaida wa manema labarai cewa, an kashe wadanda ake zargin ne a yayin da aka yi artabu a sassa daban-daban a Jihar Kaduna.

Sannan an kama wasu bisa rahotannin sirri da suka samu.

A cewar kakakin ‘yan sandan, daga cikin wadanda ake zargin akwai Auwal Saidu, wani jami’in tsaro mai zaman kansa, wanda ake zargin shi ne ya kitsa sace uban gidansa, sannan ya karbi naira miliyan 10 a matsayin kudin fansa kafin shi da ‘yan kungiyarsa su sako wanda lamarin ya rutsa da shi.

Wasu daga cikin kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da bindigogi kirar AK-47 guda biyu da babura biyu da kunshin harsashi 15 da kuma buhun tabar wiwi.

Kakakin ‘yan sandan ya bayyana cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.