✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An canza wa Ministan wasanni wajen aiki saboda fitar da Ghana

Saboda fitar da Ghana da aka yi a Gasar cin kofin duniya da ake yi a Brazil ta sa shugaban qasar John Dramani Mahama ya…

Saboda fitar da Ghana da aka yi a Gasar cin kofin duniya da ake yi a Brazil ta sa shugaban qasar John Dramani Mahama ya bayar da sanarwar canza wa Ministan harkokin wasanni da matasa da kuma mataimakinsa wajen aiki. Idan za a tuna Ghana dai ta kasa kai bantenta ne a rukunin da ta fafata da qasashen Amurka da na Fotugal da kuma Jamus a gasar cin kofin duniya a Brazil. A rukunin, Ghana ta samu rashin nasara ne a wasansu da Amurka sannan ta yi kunnen doki da ci 2-2 da Jamus yayin da Fotugal ta doke ta da ci 2-1 a da hakan ya sa aka fitar da ita tun a matakin farko. Jim kaxan bayan an fitar da qasar daga gasar ce sai shugaban qasar ya ba da sanarwa a ranar Asabar ta makon jiya cewa an canza wa Ministan kula da harkokin matasa da wasanni Elvis Afriyie-Ankrah wurin aiki daga Minista zuwa qaramin Minista a fadar shugaban qasa. Haka shi ma mataimakinsa Joseph Yamnin an koma da shi qaramin Minista mai kula da yankin Ashanti”. Sanarwar ta ce an yi waxannan canje-canje ne a qoqarin da gwamnatin Mahama take yi don farfaxo da harkokin wasanni musamman vangaren qwallon qafa a qasar. Idan za a tuna Hukumar qwallon qafar Ghana (FA) ta samu matsala da biyu daga cikin ’yan qwallon qasar watau Kevin-Prince Boateng da Sulley Muntari ana gab da yin wasa a tsakanin qasar da Fotugal a gasar cin kofin duniya a makon jiya al’amarin da ya sa aka sallami ’yan qwallon kuma suka kama gabansu tun kafin wasan ya gudana. A wasan Ghana ta samu rashin nasara ne da ci 1-2 da hakan ya sa ta kasa hayewa zagaye na biyu.