✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Abin da ya sa na taso daga gadon asibiti na zabi Buhari – Pasali

Alhaji Danladi Garba Pasali shi ne Shugaban Kungiyar Yakin Zaben Shugaban Kasa Muhammad Buhari ta Buhari Campaign Organization na Kasa. Ya bayyana dalilin da ya…

Alhaji Danladi Garba Pasali shi ne Shugaban Kungiyar Yakin Zaben Shugaban Kasa Muhammad Buhari ta Buhari Campaign Organization na Kasa. Ya bayyana dalilin da ya sanya ya taso daga kan gadon asibitin da yake jinyar harbin da barayi suka yi masa, ya je ya zabi Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Asabar da gabata:

 

Me ye ya faru game da rashin lafiya da kake yi?

Ainihin abin da ya faru shi ne a ranar Laraba 13 ga Fabarairu, mun shirya za mu bude wata cibiyar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a nan garin Jos. Wannan cibiya za ta kasance wuri ne, da za a tara bayanan ayyukan Shugaba Buhari. Ta yadda duk wanda yake son ya san ayyukan da Shugaba Buhari ya yi, cikin shekara uku da watanni da ya yi yana mulkin kasar nan, zai iya zuwa wajen ya duba.

Kuma mun shirya a wannan rana Gwamnan Jihar Filato, Simon Lalong ne zai jagoranci bude cibiyar.

Don haka na yi sammako na taso daga Abuja da misalin karfe 6 na safe, domin in halarci wannan taro. Mun zo daidai kauyen Bade da ke Jihar Kaduna, sai muka ga wata mota kirar Jeep tana bin mu a baya. Kafin mu farga sai muka ga an bude mana wuta, daga cikin wannan mota. Suka harbe ni a kafa har harsashi ya huda kafar ya fita. Shi kuma direbana suka ji masa raunuka a wurere da dama a jikinsa. Nan take na ga ya suma kuma motar tana gudu. Na rike kan motar, a haka har muka yi tafiyar kilomita daya da rabi. Da motar ta tsaya, sai na nemi taimako daga irin direbobin kananan motocin nan na Bectra da suke wucewa, suka tsaya suka taimaka mana. Aka dauke mu aka kai wani asibiti a Kwoi da ke Jihar Kaduna. Suka ba mu taimakon gaggawa, shi yaron nawa da yake ya fi ni jin raunuka, aka tafi da shi zuwa wani babban asibiti a Keffi da ke Nasarawa. Ni kuma na ce a taho da ni Jos, kuma har yanzu zancen nan da nake yi ina kwance a asibiti.

 

A ranar da aka gudanar da zaben Shugaban Kasa da ’yan Majalisar Dokoki ta Kasa mun samu labarin cewa an dauko ka daga gadon asibiti, ka je ka jefa kuri’a, me ya karfafa maka gwiwar yin haka?

Wato kai ka san wannan gwagwarmaya kan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, gwawarmaya ce da muka fara tun shekara 3 da suka gabata. Domin mun yarda da akida da rayuwarsa. Domin shi mutum ne mai gaskiya da rikon amana.

Don haka ganin cewa wannan zabe yana da muhimmanci ga al’ummar Najeriya, domin a shekara 3 da Buhari ya yi mulkin Najeriya, ya yi yaki da masu cin hanci da rashawa da ’yan ta’adda kuma ya canja akalar ’yan Najeriya daga maganar dogaro da man fetur, zuwa ga harkokin noma da sauran abubuwan da za su taimaka mana.

Shi ne ya sa na ga cewa tunda ina cikin hayyacina, sai na kira babban likitan asibitin da nake kwance, na roki a sani a mota a kai ni in je in yi zabe. Shi ne suka ba ni motar asibitin da ma’aikatansu, aka kai ni wajen da nake yin zabe na yi zabe na zabi shugaba Muhammadu Buhari.

Domin a gaskiya idan ban yi wannan zabe ba, hankalina ba zai kwanta ba. Saboda a wannan gwagwarmaya da muke yi a cikin jihohi 36 da muke da su a Najeriya, babu jihar da ba mu bude ofishi ba. Don haka na je na yi wannan zabe kuma na zauna a wajen, har kusan awa biyu na tabbatar cewa Shugaba Buhari ya lashe wannan unguwa baki daya. Domin zuwana wajen ya karfafa wa mutanen unguwar gwiwa, ganin halin da nake ciki. Don haka mutane kowa ya tashi ya shiga layi ya yi zabe.

Bayan da aka gama zaben aka kirga kuri’ar Shugaba Buhari ya samu kuri’a 776 ita kuma Jam’iyyar PDP ta samu kuri’u 8 kawai. Daga nan na koma asibitin na ci gaba da yin jinya.

 

Ganin yadda miliyoyin ’yan Najeriya suka fito wajen zabeN, duk da cewa daga farko an dage da mako daya, me kake ganin ya sanya ’yan Najeriya ba su yi sanyi ba, wajen fitowa?

Ai kamar yadda na fada maka ne tunda farko, duk dan Najeriya dan halal idan ya yi tunanin halin da Najeriya ta shiga a da inda aka rika kashe bayin Allah da sunan Boko Haram da kwashe dukiyoyin kasar nan. Aka jefa kasar ta shiga cikin mawuyacin hali. Ya zama wajibi ya mara wa Shugaba Buhari baya.

Bari in fada maka wani al’amari tunda ake siyasa a Najeriya ba a taba zaben Shugaba ba tare da ya ba da wani abu ba, sai a kansa. Shugaba Buhari bai ba wa kowa komai ba, amma duk da haka jama’a suna sonsa suna kaunarsa.

Mutanen Najeriya suna kaunar Buhari ne saboda sun san cewa mutum ne mai gaskiya kuma ya zo ya kafa harsashin gaskiya a Najeriya, don haka dole a tsaya a goya masa baya domin a tabbatar da gaskiyar ta tsaya a Najeriya.

Saboda rashin gaskiya a kasa ne ke kawo fitinu da rashin aikin yi da kashe- kashen kabilanci da addini.

 

Yaya ka ga yadda Hukumar INEC ta gudanar da zaben?

Wato wannan zabe kusan duk duniya kowa ya amince kuma kowa ya yaba wa Hukumar INEC kan yadda ta gudanar da wannan zabe mai adalci. Domin idan ka duba sakamakon zaben za ka ga babu wata tazara mai yawa tsakanin wadanda suka yi takarar.

Amma irin zaben da PDP take yi a da, zama kawai suke yi suna rubuta sakamakon zabe. Duk masu lura da zabe daga kasashen waje sun yaba. Domin an yi zabe babu tashin hankali babu fitina an bar kowa ya zabi abin da yake so.

 

A matsayinka na jigo a yakin zaben Shugaba Buhari me za ka ce kan sake zabensa da aka yi?

Dama mu ba mu taba yin kasa a gwiwa ba. Domin tuni mun yi imanin cewa Buhari zai sake cin zaben nan. Domin mutum ne mai gaskiya da rikon amana. Don haka ban taba kasa yin barci ko na kwana daya ba, kan wannan takara da Buhari ya sake fitowa. Domin na san ba zai taba yiwuwa a hada Buhari da Atiku a  takara ba, sannan a ce za a zabi Atiku. Kuma ya kamata jama’a su sani ba an kammala zaben ba ke nan, domin akwai masu ra’ayin cewa su Buhari kawai za su zaba. Don haka muna kira ga jama’a su fito su zabi gwamnoni da ’yan majalisun jihohi. Domin idan Buhari bai samu ma’aikata ko abokan aiki ba, ba zai iya aiki shi kadai ba. Don haka mu kara daura damara mu fito mu zabi gwamnoninmu da ’yan majalisunmu na jihohi.

 

Wasu daga cikin zababbun sanatoci da

Hukumar INEC ta sanar

 

Kwara Central

Ibrahim Y. Oloriegbe (APC) 123,808 – Winner

Bukola Saraki (PDP) 68,994

Kwara South

Lola Ashiru (APC) 89, 704 – Winner

Rafiu Ibrahim (PDP) 45,176

Kwara North

Umar Sadik (APC) 98170 – Winner

Zakari Mohammed (PDP) 33, 364

Benue South

Abba Moro (PDP) 85,162 – Winner

Steben Lawani (APC)47,972

Benue South

Abba Moro (PDP) 85,162 – Winner

Steben Lawani (APC)47,972

Kogi West

Dino Melaye (PDP) 85, 395 – Winner

Smart Adeyemi (APC) 66,901

Kogi Central

Yakubu Oseni (APC) 76,120- Winner

Natasha Akpoti (SDP) 48,326

Borno South

  1. Ali Ndume (APC) 301,312 – Winner

Kulda Sarunmari (PDP) 84,692

Jigawa North

Ibrahim H. Hadeija (APC) 184,185 – Winner

Ubale Shittu (PDP) 103,039

Jigawa North-West

Danladi Sankara (APC) 286,655 – Winner

Nasiru Roni (PDP) 120,314

Jigawa Central

Sabo Nakudu (APC) 224,543 – Winner

Mustapha Sule Lamido (PDP) 143,611

Edo North

Francis Alimekhena (APC) 117,783 – Winner

Abubakar Momoh (PDP) 80,752

Abia North

Orji Uzor Kalu (APC) 30,580 – Winner

Mao Ohuabunwa (PDP) 21,940

Kano Central

Ibrahim Shekarau (APC) 506,271

Aliyu Sani Madaki (PDP) 267,778

Kano South

Kabiru Gaya (APC) 319,004 – Winner

Abdullahi Sani Rogo (PDP) 217,529

Kano North

Jibrin Barau (APC) 286,419 – Winner

Ahmad Bichi (PDP) 155,638

Kano North

Jibrin Barau (APC) 286,419 – Winner

Ahmad Bichi_ (PDP) 155,638

Nasarawa West

Abdullahi Adamu (APC) 115,298 – Winner

Bala Ahmed Aliyu (PDP) 85,615

Nasarawa North

Umaru T. Almakura (APC) 113,156 – Winner

Suleiman Adokwe (PDP) 104,595

Oyo South

Kola Balogun (PDP) 105,720 – Winner

Abiola Ajimobi (APC) 92,218

Gombe Central

Danjuma Goje (APC) 110,116 – Winner

Nasiru Abubakar Nono (PDP) 39,155

Gombe North

Saidu Ahmed Alkali (APC) 152,546 – Winner

Hassan Dankwambo (PDP) 88,016

Gombe South

Amos Bulus (APC) 80,549 – Winner

Binta Bello (PDP) 63,312

Kaduna South

Danjuma La’ah (PDP) 268,287 – Winner

Bala Banted (APC) 133,923

Kebbi South

Bala Ibn Na’allah (APC) 136,187 – Winner

Benjamin Wikki (PDP) 62,733

Osun West

Lere Oriolowo (APC) 102147 – Winner

Lere Oyewumi (PDP) 97,294

Niger North

Aliyu Sabi Abdullahi (APC) 161,420 – Winner

Muhammad Sani Duba (PDP) 77,109

Table UKEOMA MODESTUS

 

Wasu daga cikin zababbun sanatoci da

Hukumar INEC ta sanar

East

Sani Musa (APC) 229,415 – Winner

Ishaku Ibrahim (PDP) 116,143

Niger South

Bima M. Enagi (APC) 160,614 – Winner

Shehu Baba Agaie (PDP) 90,978

Yobe South

Ibrahim M. Bomo (APC)118,729 – Winner

Mohammed Hassan (PDP) 89,049

Yobe North

Ahmad Lawan (APC) 144,099 – Winner

Sheriff Abdullahi (PDP) 53,443

Yobe East

Ibrahim Geidam (APC) 139,277 – Winner

Abba Gana Tata (PDP) 18,059

Ondo Central

Ayo Akinyelure (PDP) 67,994_ – Winner

Tayo Alasoadura (APC) 58,092

Wasu daga cikin zababbun sanatoci da

Hukumar INEC ta sanar

Imo west

Rochas Okorocha (APC) 97,762 – Winner

Jones Onyereri (PDP) 63,117

Akwa Ibom South

Akon Eyakenyi (PDP) 122,412 – Winner

Nelson Effiong (APC) 44,053

Katsina Central

Kabir Barkiya (APC) 340,800 – Winner

Hamisu Gambo Danlawan (PDP) 124,372

Katsina North

Ahmad Babba Kaita (APC) 339,438 – Winner

Mani Nasarawa (PDP) 127,52

Katsina South

Bello Mandiya (APC) 433,139 – Winner

Imam Shehu Inuwa (PDP) 158,081

Ogun Central

Ibikunle Amosun (APC) 88,110 – Winner

Titi Oseni-Gomez (ADC) 37,101

Ekiti South

Dayo Adeyeye (APC) 77,621 – Winner

Biodun Olujimi (PDP) 53,741

Ekiti Central

Opeyemi Bamidele (APC)94,297 – Winner

Obafemi Adewale (PDP) 46, 707

Ekiti North

Olubunmi Adetunbi (APC) 60,689 – Winner

Duro Faseyi (PDP) 49,209

Adamawa North

Ishaku Cliff (PDP) 43,117 – Winner

Binta Masi Garba (APC) 16,219

Adamawa Central

Aishatu Dahiru (APC) 188,526 – Winner

Mohammed Chubado (PDP) 96, 530

Osun Central

Ajibola Bashiru (APC) 132,821 – Winner

Ganiyu Olaoluwa 106,779

Ebonyi North

Sam Egwu (PDP) 80,711 – Winner

Mathias Adum (APC) 38,374

Ebonyi Central

Obinna Ogba (PDP) 62,452 – Winner

Julius Ali-Ucha (APC) 46,676

Ebonyi South

Michael Ama Nnachi (PDP) 103,751 – Winner

Prince Nweze Onu (APC) 19,663

Akwa Ibom North-East

Bassey Albert (PDP) 147,731- Winner

Bassey Etim (APC) 60, 930.

Anambra Central

Uche Ekwunife (PDP) 18,412 – Winner

Bictor Umeh (APGA) 14,403

Osun East

Adenigba Fadahunsi (PDP) 114,893 – Winner

Ajibola Famurewa (APC) 105,720

Lagos West

Solomon Olamilekan (APC) 23,189 – Winner

Mr Gbadebo Rhodes (PDP) 16,248

Lagos Central

Oluremi Tinubu (APC) 131,735 – Winner

Onitiri Dabid (PDP) 89,107