✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zulum ya ba iyalan Janar din sojan da aka kashe a Borno N20m

Zulum da sanatocin jiharsa sun jajanta wa iyalan sojojin da suka rasu a harin ISWAP.

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya kai ziyarar ta’aziya ga iyalan marigayi Birgediya-Janar Dzarma Zirkusu wanda mayakan kungiyar ISWAP suka kashe a Jihar Borno.

A ranar Laraba ce gwamnan jagoranci daukacin sanatocin jihar masu ci, zuwa gidan mamacin da ke barikin sojoji na Ribadu da ke Kaduna, inda , inda suka jajanta musu, ya kuma ba su tallafin Naira miliyan 20.

Mai magana da yawun gwamnan, Isa Gusau, ya sanar da cewa gwamnan zai kuma bayar da kwatankwacin tallafin ga iyalan kananan sojoji uku da suka kwanta dama tare da Janar Dzarma a musayar wutar da suka yi da ’yan ta’addan.

Zulum lokacin da ya ziyarci iyala sojan a Kaduna
Zulum tare da babban dan mamacin, a lokacin da ya ziyarci iyalan Janar Dzarma Zirkusus a gidansu da ke Kaduna.

Zulum ya kai ziyarar ta’aziyyar a Kaduna ne tare da ’Yan Majalisar Dattawa Jihar Borno masu ci, da kuma ’yan Majalisar Dokokin Jihar Borno biyu, masu wakiltar mazabar Chibok da Askira Uba, inda Janar Dzarma da dakarun nasa suka gamu da ajalinsu.

‘Ya’yan Janar Dzarma biyar a lokacin ta’aziyyar da Gwamna Zulum ya kai musu.

A lokacin ziyarar, gwamnan ya gana da mai dakin Janar Dzarma da ’ya’yansa biyar da kuma dan uwan mamacin, inda ya jajanta musu gami da yaba wa jarumtar mamatan.

Babban Kwamandan Runduna ta Daya ta Sojin Kasan Najeriya, Birgediya-Janar T. Opuene tare da Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, su ne suka tarbi Zulum da tawagar tasa, kafin suka zarce zuwa gidan marigayin.