✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBC

Kotun ta ware ranar 3 ga watan Yuni, 2025 a matsayin ranar da za ta yanke hukunci kan taƙaddamar.

Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta sanya ranar 3 ga watan Yuni, 2025 domin yanke hukunci kan shari’ar BBC da mawaƙi Abdul Kamal.

Tunda farko Abdul, ya maka kafar ne a kotu, inda yake neman ta biya shi diyyar Naira miliyan 120, kan zargin amfani da waƙarsa a shirinsu na “Daga bakin mai ita” ba tare da izininsa ba.

A zaman shari’ar na ranar Litinin, lauyan mai ƙara, Barista Bashir Ibrahim Umar, ya gabatar da makaɗin waƙar, Muhammad Sani Uba a matsayin ɗaya daga cikin shaidun wanda ke ƙara.

Makaɗin ya tabbatar wa kotu cewa shi ne, ya yi wa Kamal kiɗan da ake shari’ar a kansa.

Daga bisani alƙalin kotun, ya sanya ranar 3 ga watan Yuni, 2025 domin yanke hukunci kan shari’ar.