✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Zaben Adamawa: An kasa gurfanar da Hudu Yunusa-Ari a kotu

Yunusa Ari ya yamutsa hazo bayan da ayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan Adamawa ana tsaka da kirga kuri'u

An gaza gurfanar da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa na Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da aka dakatar, Hudu Yunusa Ari a gaban babbar kotun jihar a yau Litinin.

Hakan ya biyo bayan gazawar ’yan sanda su sanar da Yunusa-Ari sauraron kararsa a gaban da ke zamanta Yola, hedikwatar jihar.

A cewar lauyan masu shigar da kara, Rotimi Jacobs, ’yan sandan sun kai takardar karar ta hanyar ziyartar gidansa amma a cikin takardar ba a bayyana hakikanin wanda ake tuhuma ba.

Alkalin kotun, Benjamin Manji, ya yi mamakin dalilin da ya sa ’yan sandan da suka bayar da belinsa suka gaza gurfanar da shi a gaban kotu ko kuma wakilinsa.

Don haka, ya amince da bukatar lauyan masu gabatar da kara da wanda ake kara ya bayyana a gaban kotu a zama na gaba.

Daga nan ya umarci INEC ta gurfanar da shi a gaban kotu a zamanta na gaba ranar 23 ga Nuwamba, 2023.

Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala zaman, lauyan INEC, Rotimi Jacobs, ya tabbatar da cewa za a yi duk yiwuwa don ganin wanda ake kara ya bayyana a zama na gaba.

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta bai wa INEC damar gurfanar da Yunusa-Ari wanda ke fuskantar tuhume-tuhume shida kan rawar da ya taka wajen bayyana sakamakon bogi a zaben gwamnan jihar Adamawa na 2023.

Bayan kammala zaben gwamnan a ranar 15 ga watan Afrilu, Ari da aka dakatar ya ayyana ’yar takarar APC, Sanata Aishatu Binani a matsayin wadda ta yi nasara a lokacin da ake tsaka da tattara sakamakon zaben.

Matakin nasa ya haifar da rudani, inda INEC ta yi watsi da sanarwar tare da dakatar da shi nan take.