✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a yi jana’izar alhazan kasar Jordan 41 a Makkah

Ana ci gaba da neman sauran mahajjatan kasar Jordan 22 daga cikin 106 da suka bata a Saudiyya

Gwamnatin kasar Jordan ta ce za a gudanar da jana’izar alhazan kasar guda 41 a birnin Makkah, bayan sun rasu a sakamakon tsananin zafi a lokacin aikin hajji a kasar Saudiyya.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jordan, Sufian Qudah, ya sanar cewa kasar an gano 84 daga cikin alhazan kasar 106 da suka bace a Saudiyya.

Qudah ya bayyana cewa hukumomin Saudiyya sun ba da kulawar da ta dace ga alhazan 84, wadanda wasunsu ke cikin mawuyacin hali.

Ya kara da cewa, ofishin jakadancin kasar da ke Makka na kara ba da kula tare da sanya ido kan halin da alhazan ke ciki tare da hadin gwiwan hukumomin Saudiyya.

Kakakin ya ci gaba da cewa har yanzu ana ci gaba da neman sauran alhazan kasarsa 22 da suka bata.

Daga nan ya yi kira ga dukkan ’yan kasar da ke Hajji da su tuntubi ma’aikatar idan ana bukatar taimako, ciki har da kai rahoton wadanda suka bace ko kuma jigilar gawarwakin, idan sun mutu.