✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a yi fama da hazo da kura a jihohin Arewa a kwanaki masu zuwa – NiMet

NiMet ta shawarci masu ababen hawa da su yi tuki cikin nutsuwa.

Hukumar Hasashen Yanayi ta Najeriya (NiMet), ta sanar da karewar yanayin damina a Arewacin kasar nan, inda ta ce wasu sassan yankin za su fuskanci yanayin kura da hazo nan da kwanaki masu zuwa. 

NiMet a hasashenta ta ce kura za ta taso daga jamhuriyar Nijar kuma za ta mamaye sassan Arewacin na Najeriya.

Guguwar iska mai karfin mita 800, a cewar NiMet, za ta kai kurar zuwa Arewacin kasar nan da kuma Arewa ta Tsakiya.

Binciken ya kuma nuna cewa ana sa ran za a samu karin kura da hazo a yankin.

“A cikin sa’o’i 24 masu zuwa, akwai yiwuwar karin hazo da kura (a matsakaicin nisan zango mita 2000 – mita 5000) a jihohin Borno, Yobe, Katsina, Kano, Kaduna, Gombe, Bauchi da Jigawa, yayin da sauran jihohin Arewa (ciki har da Arewa ta Tsakiya) na iya fuskantar yanayin zafi kan mataki 5-7.

“Ana sa ran wannan yanayin zai ci gaba har zuwa kwanaki uku masu zuwa.”

NiMet ta kuma ce yawan zafin rana zai karu a hankali.

Hukumar ta shawarci masu ababen hawa da su rika yin tuki cikin natsuwa a wannan yanayi.

“Hakanan mutanen da ke da matsalar numfashi ya kamata su yi taka tsantsan, musamman a lokutan da suke waje,” inji NiMet.

Ta kuma shawarci ma’aikatan jirgin sama da su nemi sabbin rahotannin yanayi daga ofisoshinta don inganta ayyukansu.